BBC News, Hausa - Labaran Duniya
Babban Labari
KAI TSAYE, Hezbollah ta ce ta harba rokoki kan garuruwa da dama na Isra'ila
Wannan shafi na kawo muku abubuwan da ke faruwa a yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi da Iran da kuma sauran muhimman labarai a sassan duniya na 16/04/2026.
Jerin jihohi da biranen Najeriya da ambaliya za ta shafa a 2026
An bukaci gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi da hukumomin bayar da agajin gaggawa da manoma da shugabannin al'umma da su dauki matakan gaggawa da suka dace domin shirya wa ambaliyar.
Ƙasashen duniya da tattalin arziƙinsu zai fi haɓaka a 2026
Bayan rashin tabbas da tattalin arziƙin duniya ya fuskanta a shekarar da ta gabata, tattalin arziƙin ya sake gamuwa da cikas sanadiyyar rikicin da ake fama da shi a Gabas ta Tsakiya.
Zarge-zargen da ake yi wa shugaban INEC - Ko za su shafi zaɓen Najeriya na 2027?
Kusan wannan ne karon farko da wani shugaban hukumar zaɓen Najeriya ke fuskantar ƙalubale daga shugabannin jam'iyyun da na addinai da kuma sauran al'umma.
Wasu Iraniyawa na cikin fargaba bayan gaza cimma yarjejeniya
Tsagaita wutar da ke tsakanin Amurka da Iran wadda take sama take ƙasa ta ƙara jefa wasu mutane musamman masu rauni da waɗanda ba sa goyon bayan jajircewar da ƙasar tasu ta Iran ke yi, cikin zaman ɗar-dar bayan tattaunawar zaman lafiya da aka yi tsakanin ɓangarorin biyu a Pakistan ta ƙare ba tare da cimma wata matsaya ba.
Liverpool na harin Senesi, City na son Read, Newcastle na zawarcin Mourinho
Liverpool na harin ɗan wasan Bournemouth Marcos Senesi, ya yin da suke kuma son ɗauko Anthony Gardon, sai Manchester City da ke son siyen ɗan wasan baya na Feyenoord Givairo Read.
Tattaunawa tsakanin Amurka da Iran na tafiya yadda ya kamata - Fadar White House
Wannan shafi na kawo muku sahihan bayanai dangane da wainar da ake toyawa a yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi da Iran da kuma sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya 15/04/2026
Ko Trump zai yi nasara kan toshe tashoshin ruwan Iran?
Matakin na Trump yana da tasiri amma sai a nan gaba za a ga wa matakin zai fi shafa a bayyane.
Me korar da ADC ta yi wa Nafi'u Bala ke nufi?
Jam'iyyar ADC mai adawa ta sanar da korar tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar wanda ke ikrarin shi ne halastaccen shugabanta, Nafi'u Bala Gombe tare da wasu ƴan jam'iyyar da ke kiran kansu jagororin jam'iyyar
Shirye-shiryenmu
Saurari na gaba, Shirin Rana, 13:59, 16 Aprilu 2026, Tsawon lokaci 30,00
Shiri ne na minti 30 wanda ya kunshi labaru da rahotanni daga sassa daban-daban na duniya.
Saurari, Shirin Hantsi, 06:30, 16 Aprilu 2026, Tsawon lokaci 29,30
Shiri ne na minti 30 wanda ya kunshi labaru da rahotanni daga sassa daban na duniya.
Saurari, Shirin Safe, 05:29, 16 Aprilu 2026, Tsawon lokaci 30,00
Shiri ne na minti 30 wanda ya kunshi labaru da rahotanni daga sassa daban na duniya.
Saurari, Shirin Yamma, 19:29, 15 Aprilu 2026, Tsawon lokaci 30,00
Shiri ne na minti 30 wanda ya kunshi labaru da rahotanni daga sassa daban-daban na duniya.
Wasanni
KAI TSAYE, Arsenal ta kai wasan kusa da ƙarshe, Bayern ta zazzaga wa Madrid ƙwallaye
Wannan shafi ne da zai ke kawo muku labaran wasannin BBC Hausa daga ranar Lahadi 12 zuwa Juma'a 18 ga watan Afrilun 2026.
Me ya sa manyan ƙungiyoyin Ingila ke shan wahala a hannun 'ƙanana'?
Har yanzu magoya bayan Manchester United na cikin alhinin rashin nasara da ƙungiyar ta yi a wasanta da Leeds United ranar Litinin da maraice.
Lokuta bakwai da manyan ƙungiyoyin Premier suka yi 'dakon teburi'
Yayin da Arsenal ke neman kore taken da ake yi mata na mai "dakon teburi", mun duba wasu lokuta a baya da manyan ƙungiyoyin Premier suka gaza kai bantensu bayan an kyautata musu zato.
Sakamakon wasannin ƙarshen mako: Arsenal da Real sun yi tuntuɓe
Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran wasannin BBC Hausa daga ranar Talata 7, zuwa Asabar 11 ga watan Afrilun 2026.
Wane mai tsaron raga ne ya fi tashe a wannan lokaci?
David Raya da Manuel Neuer sun nuna hazaƙa a wasannin gasar Champions League da ƙungiyoyinsu suka buga a baya-bayan nan - to amma ko suna cikin mafiya hazaƙa a duniya?
Tashar WhatsApp ta BBC Hausa
A wannan shafin za ku samu labarai daga ƙasashen Afrika da kuma sauran sassan duniya da ɗumi-ɗuminsu domin masu bibiyar mu a WhatsApp.
Kashe ƙwarƙwatar ido
Kuna son tattalin datarku?
Shiga shafinmu na labarai maras hoto domin rage zuƙar data
Labarai da Rahotanni Na Musamman
Me ya sa cutar ƙyanda ke saurin yaɗuwa?
Wannan cuta mai matuƙar saurin yaɗuwa na iya haifar da matsaloli masu tsanani, har ma ta kai ga mutuwa. Yin rigakafi shi ne hanya mafi inganci wajen hana ɓarkewar cutar.
Yadda cacar baki ta kaure tsakanin Donald Trump da Fafaroma Leo
Dangantaka tsakanin Fadar Vatican da Fadar White House ta dade tana ƙara yin sanyi na tsawon watanni da dama kafin Fafaroma Leo XIV ya fara sukar Donald Trump kai tsaye kan yaki a Iran.
Lokuta biyar da Boko Haram ta 'kashe' manyan sojojin Najeriya a 2026
Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da mutuwar wani babban kwamandanta da ke jagorantar sansaninta na Munguno a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya, a wani harin Boko Haram.
Matsalar tsaro: Maƙarkashiya ake yi wa Tinubu - Akpabio
''Ina tabbatar ma, Shugaban Kasa, mako biyu bayan ka ci zaɓen (2027), za a daina kai harin bambamai. Mutane na ɗaukar nauyin kai harin ne domin kawar da hankalinka daga aikin da kake yi.''
Yadda aka gano asibitocin da ke yaɗa wa yara cutar HIV - Binciken BBC
An ɗauki bidiyon jami'an lafiya na amfani da sirinji ɗaya wajen yi wa yara da dama allura kuma suna aiki ba tare da sanya safar hannu ta kariya ba, sai dai shugaban asibitin ya ƙi amincewa da sahihancin bidiyon.
Akwai yiwuwar sake tattaunawa tsakanin Amurka da Iran - Trump
Wannan shafi na kawo muku sahihan bayanai dangane da wainar da ake toyawa a yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi da Iran da kuma sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya
Abin da ya kamata ku sani kan taron Jam'iyyar ADC na ƙasa
Jam'iyyar ADC ta haɗakar masu hamayya a Najeriya ta ce ta kammala shirinta tsaf, domin gudanar da babban taronta na ƙasa a Abuja, babban birnin ƙasar.
Me ya sa Fafaroma Leo zai kai ziyara masallaci?
Fafaroma Leo XIV na ziyara a nahiyar Afirka, wadda ita ce mafi tsawo da zai yi tun bayan hawa kan muƙamin.
Yadda yaƙin Iran zai sanya ƙasashe rige-rigen mallakar makamin nukiliya
A cewar masana yaɗuwar makaman nukiliya da BBC ta tattauna da su, idan aka duba halin da ake ciki yanzu, ba gwamnatin Iran kaɗai ba ce za ta yi tunanin cewa mallakar makamin nukiliya shi ne hanyar kare kai, har ma da wasu ƙasashen.
Yadda aka ba Fulani wa'adi su bar wasu garuruwa a jihar Kwara
''Fulaninmu da ke yankin gaba daya an ba mu kwana biyu zuwa uku, an ce mu tashi, kuma duk wanda bai tashi ba an ce to yana cikin matsala kuma duk abin da ya same shi to ya kuka da kanshi.''
Jirgin ruwa ya ratsa ta mashigar Hormuz duk da barazanar Trump
Wannan shafi na kawo muku sahihan bayanai dangane da wainar da ake toyawa a yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi da Iran da kuma sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya
Me ya sa gwamnan Kano ke jan ƙafa kan naɗin mataimakinsa?
Yanzu an kwashe kusan mako uku tun bayan da tsohon mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdussalam ya sauka daga muƙaminsa bayan rikicin siyasa da ya turnuƙe sanadiyyar sauya sheƙar gwamnan jihar zuwa APC mai mulki a Najeriya.
KAI TSAYE - Labaran BBC Hausa
Saurari labaran BBC Hausa Kai Tsaye Litinin zuwa Juma’a da karfe 0530, 0630, 1400 da 1930 GMT, sai kuma Asabar da Lahadi da karfe 0530, 0630 da 1930 GMT.
































































