A shirye nake na zaune da 'yan hamayya don ceton Zamfara

Bayanan bidiyo, Gwamnan Jihar Zamfara
An wallafa

Gwamnan Zamfara Dr Dauda Lawan Dare ya yi kira ga abokan hamayyarsa su zo a sa Zamfara gaba domin ciyar da ita gaba bayan hukuncin kotun koli da ya tabbatar da nasararsa ta gwamna.

Gwamna Dauda ya ce a shirye yake ya zauna da abokin hamayyarsa tsohon gwamna kuma karamin ministan tsaro Dr Bello Muhammad Matawalle kan matsalar tsaron da ta addabi jihar.

A hirarsu da BBC Gwamna Dauda ya ce bai taba shakkun rashin nasara ba a kotun koli domin a cewarsa sahihin zabe aka gudanar, amma ya fara da bayyana farin cikinsa game da hukuncin.